الأربعاء، 9 يناير 2019

معنى البدعة (Ma'anar Bidi'a)

BIDI'A BA MA'AUNIN AUNA AYYUKAN WADANDA BA MUSULMI BA NE..

Duk da dai ma'aunin da kuke amfani da shi a ma'anar Bidi'a a fahimtar ku ya sha bamban da wanda malamai -a fahimta ta- suke amfani da shi, duk da haka, ma'anonin duka biyu -da nawa da naka - ba za su yi aiki a nan ba, Saboda akwai aya a Alkur'ani Mai girma da take nuna cewa Allah bai zargi Kiristoci akan kirkirar ibada ba, bal ma, sigar ayar ta zo ne a siyaq din goranta masu ni'imomin da Allah ya yi masu, laifin su, ba shi ne kirkirar ibadar da ba a yi masu umurni ba, a'a, laifinsu kawai shi ne : bayan sun kirkiri ibadun, sun kasa lizimta akan su, sun kasa cigaba da aikata abin da suka kirkira.. Ga dai ma'anar ayar .

Allah Madaukakin Sarki a cikin suratul Hadid aya ta 27 yana cewa : ((.. Sannan muka turo wasu Manzannin mu a bayan su, muka turo Isah dan Maryam, muka ba shi Injila, muka sanya jinkai da tausayi a cikin zukatan wadanda suka bi shi, da kuma son ibadar - da su ne suka kirkiro su domin neman yardar Allah-, sai dai ba su kiyaye wannan ibada kamar yadda ta kamata ba, sai muka bai wa wadanda suka yi imani daga cikin su ladansu, amma mafi yawan cikinsu masu saba wa umurnin Allah ne..))

Saboda haka, idan Kiristoci sun kirkiri Bikin Kirsimeti domin tunawa da Annabi Isah AlaiHis salam, suka kuma yi ibadu a wannan lokacin, hakan ba zai zama Bidi'a ba har a irin ma'anar da ku kuke bai wa Bidi'a, wanda da ma na fadi cewa ya sha bamban da irin yanda na fahimci ma'anar Bidi'a a karatun da na yi a gaban malamai..

Muna taya abokan zaman mu, kuma 'yan uwanmu a cikin mutumtaka, da kasa daya, wato Kiristoci murna da wannan lokaci ne domin sauke nauyin da Allah ya daura mana a cikin suratul Mumtahana aya ta 8, inda ya nemi da mu kyautata masu, mu kuma yi masu adalci, saboda Allah yana son masu adalci..

Ya kamata bal ya wajaba mu kyautata masu, mu kuma yi masu adalci domin Allah ya so mu..

Abin da zai hana mu yi masu haka kawai shi ne idan sun yake mu saboda da addini -ba saboda rikicin kabilanci ba-, suka kuma fitar da mu daga gidajen mu saboda da kin su da addinin Musulunci -shi ma ba saboda kabilanci ba- to in dai har suka yi mana haka, to babu batun taya murna..

Allah shi ne Masani..

Saleh Kaura

(C) TASAKR SUNNA

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق